
Tun daga ranar 1 ga Mayu, 2026, kasar Sin za ta aiwatar da cikakken matakan rage haraji ga kasashe 53 na Afirka wadanda ke da huldar diflomasiyya da su. A lokaci guda kuma, za ta ci gaba da tallata sanya hannu kan yarjejeniyar hadin gwiwa kan tattalin arziki don ci gaba tare da kara fadada damar da kayayyakin Afirka ke samu zuwa kasar Sin ta hanyar inganta "tashar kore" da sauran matakai.